Hausa
Surah Al-Balad ( The City ) - Aya count 20
لَا أُقْسِمُ بِهَٰذَا الْبَلَدِ
( 1 ) 
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلٌّ بِهَٰذَا الْبَلَدِ
( 2 ) 
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ
( 3 ) 
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي كَبَدٍ
( 4 ) 
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ
( 5 ) 
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا
( 6 ) 
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُ أَحَدٌ
( 7 ) 
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُ عَيْنَيْنِ
( 8 ) 
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ
( 9 ) 
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيْنَاهُ النَّجْدَيْنِ
( 10 ) 
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلَا اقْتَحَمَ الْعَقَبَةَ
( 11 ) 
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْعَقَبَةُ
( 12 ) 
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍ
( 13 ) 
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍ
( 14 ) 
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ
( 15 ) 
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ
( 16 ) 
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا بِالْمَرْحَمَةِ
( 17 ) 
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ
( 18 ) 
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَالَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِنَا هُمْ أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ
( 19 ) 
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌ
( 20 ) 
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.