Hausa
Surah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Aya count 25
إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ
( 1 ) 
Idan sama ta kẽce,
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
( 2 ) 
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ
( 3 ) 
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
( 4 ) 
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
( 5 ) 
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ
( 6 ) 
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ
( 7 ) 
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
( 8 ) 
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰ أَهْلِهِ مَسْرُورًا
( 9 ) 
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ
( 10 ) 
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا
( 11 ) 
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
( 12 ) 
Kuma ya shiga sa'ĩr.
إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا
( 13 ) 
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
( 14 ) 
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَىٰ إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا
( 15 ) 
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ
( 16 ) 
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
( 17 ) 
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ
( 18 ) 
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
( 19 ) 
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
( 20 ) 
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
( 21 ) 
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا يُكَذِّبُونَ
( 22 ) 
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
( 23 ) 
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
( 24 ) 
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ
( 25 ) 
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.