Hausa
Surah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) - Aya count 40
لَا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ 
( 1 ) 
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
وَلَا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِ 
( 2 ) 
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُ 
( 3 ) 
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
بَلَىٰ قَادِرِينَ عَلَىٰ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُ 
( 4 ) 
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
بَلْ يُرِيدُ الْإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُ 
( 5 ) 
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ 
( 6 ) 
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُ 
( 7 ) 
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
وَخَسَفَ الْقَمَرُ 
( 8 ) 
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ 
( 9 ) 
Aka tãra rãnã da watã
يَقُولُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّ 
( 10 ) 
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
كَلَّا لَا وَزَرَ 
( 11 ) 
A'aha! bãbu mafaka.
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّ 
( 12 ) 
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
يُنَبَّأُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ 
( 13 ) 
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
بَلِ الْإِنسَانُ عَلَىٰ نَفْسِهِ بَصِيرَةٌ 
( 14 ) 
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُ 
( 15 ) 
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
لَا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِ 
( 16 ) 
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُ 
( 17 ) 
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُ 
( 18 ) 
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُ 
( 19 ) 
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَ 
( 20 ) 
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
وَتَذَرُونَ الْآخِرَةَ 
( 21 ) 
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ 
( 22 ) 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ 
( 23 ) 
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌ 
( 24 ) 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ 
( 25 ) 
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
كَلَّا إِذَا بَلَغَتِ التَّرَاقِيَ 
( 26 ) 
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ 
( 27 ) 
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُ 
( 28 ) 
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِ 
( 29 ) 
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُ 
( 30 ) 
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ 
( 31 ) 
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ 
( 32 ) 
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰ أَهْلِهِ يَتَمَطَّىٰ 
( 33 ) 
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ 
( 34 ) 
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ 
( 35 ) 
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًى 
( 36 ) 
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىٰ 
( 37 ) 
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ 
( 38 ) 
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ 
( 39 ) 
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىٰ 
( 40 ) 
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?