Hausa
Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya count 46
وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا 
( 1 ) 
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا 
( 2 ) 
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا 
( 3 ) 
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا 
( 4 ) 
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا 
( 5 ) 
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ 
( 6 ) 
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ 
( 7 ) 
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ 
( 8 ) 
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ 
( 9 ) 
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ 
( 10 ) 
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً 
( 11 ) 
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ 
( 12 ) 
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ 
( 13 ) 
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ 
( 14 ) 
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ 
( 15 ) 
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى 
( 16 ) 
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ 
( 17 ) 
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ 
( 18 ) 
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ 
( 19 ) 
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ 
( 20 ) 
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ 
( 21 ) 
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ 
( 22 ) 
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ 
( 23 ) 
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ 
( 24 ) 
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ 
( 25 ) 
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ 
( 26 ) 
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا 
( 27 ) 
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا 
( 28 ) 
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا 
( 29 ) 
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا 
( 30 ) 
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا 
( 31 ) 
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا 
( 32 ) 
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ 
( 33 ) 
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ 
( 34 ) 
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ 
( 35 ) 
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ 
( 36 ) 
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ 
( 37 ) 
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا 
( 38 ) 
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ 
( 39 ) 
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ 
( 40 ) 
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ 
( 41 ) 
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا 
( 42 ) 
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا 
( 43 ) 
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا 
( 44 ) 
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا 
( 45 ) 
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا 
( 46 ) 
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.